Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Ganduje ya rabawa likitoci kayan kare kai daga Corona

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta bukaci asibitoci masu zaman Kansu dasu daina mayar da marasa lafiya gida idan sun zo asibitocin su.

Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ne ya bayyana hakan a yau lokacin da yake zagayawa asibitoci masu zaman kansu yana raba kayan kariyar jamian lafiya da feshin magani.

Gwamna Ganduje ya kara da jan hankalin su akan su yi amfani da kayan kariyar Don kariyar kansu da kuma sanar wa da gwamnatin duk wanda aka Gani yana da alamun Corona

Karin labarai:

Yanzu-yanzu: Ganduje ya fara rabon tallafin Corona

Za a rika bude Kano sau biyu a sati -Ganduje

Da yake jawabi shugaban tawagar kwamitin ministan lafiya a Kano Dr Nasir Sani Gwarzo lokacin da Gwamnan ya ziyarci inda kwamitin ke horar da jamian lafiya ya ce a yanzu haka sun gano matsalar Kano kan cutar Corona kuma suna dab da cimma nasara.

Wakiliyar mu Zahrau Nasir ta ruwaito cewa  asibitocin da Gwamnan ya ziyarta don kai tallafin Kayan kariyar da kuma feshin magani sun hada da Asibitin idanu na Makka da asibitin Al’amin medical center da asibitin Standard specialist hospital.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!