Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Covid-19: Gobe ranar sassauta dokar kulle a Kano

Published

on

Gwamnatin jihar Kano tace gobe Alhamis za a sassauta dokar kulle da zaman gida a jihar kamar yadda aka saba domin baiwa al’umma damar sayen kayan abinci.

Maitaimakawa gwaman Kano na musamman kan yada labarai Salihu Tanko Yakasai ne ya bayyana hakan, a zantawarsa da wakilin mu Aminu Bello.

Salihu Yakasai na martani ne kan rahotonnin da ake yadawa cewa a ranar Alhamis babu sararawa saboda tsawaita dokar kulle da gwamnatin Kano tayi a ranar Litinin.

Labarai masu alaka:

Ganduje ya amince a rika bude mayankar “Abbatuwa” a ranakun sararawa

Ganduje ya kaddamar da rabon “Face Mask” miliyan biyu ga Kanawa

Idan zaku iya tunawa dai a kwanakin baya ne gwamnatin Kano ta amince da ranakun Litinin da Alhamis da karfe 10 na safe zuwa karfe 4 na yamma domin sararawa ga al’umma.

Tuni dai gwamatin ta Kano ta kaddamar da rabon amawalin rufe baki da hanci ga jama’a, bayan da ta sanya dokar tilasta amfani dashi a jihar domin dakile cutar Covid-19.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!