Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ganduje ya musanta komawa makarantu ranar 14 ga watan Yuni

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta musanta labarin da ake yadawa cewa ta amince a koma makarantu a ranar 14 ga waan da muke ciki.

Kwamishinan ilimi na jihar Kano, Malam Muhammad Sanusi Sa’idu Kiru ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun jami’in hulda da jama’a na ma’aikatar Aliyu Yusuf a jiya Lahadi.

Sanarwar ta ce, labarin da ke yawo a shafukan sada zumunta kan komawa makaranta ba gaskiya bane.

Ganduje ya haramta amfani da injin Janareto a Kasuwar Sabon Gari

Ganduje zai dasa Bishiyu miliyan biyu domin kiyaye zaizayar kasa

Idan dai za a iya tunawa tun a watan Maris ne gwamnonin jahohin kasar nan suka dauki matakin rufe makarantu sakamakon barkewar annobar Covid-19 a kasar nan.

Sanarwar ta kuma bukaci iyaye da malaman makarantu da su kara hakuri, tana mai cewa tuni tattaunawa tayi nisa tsakanin gwamnatin tarayya da ta jiha kan shirye-shiryen tsara yadda komawar dalibai makaranta zata kasance kan ka’idojin kula da lafiya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!