Labarai
Gobara ta lakume kasuwar Takumbo da wasu gine-gine a Kano

Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano ta ce gobara mai tsanani ta tashi a daren ranar 11 ga Yuni, 2026, a kan titin Murtala Mohammed Way kusa da bankin FCMB a karamar hukumar Fagge.
A cewar sanarwar da jami’in hulda da jama’a na hukumar, ACFO Saminu Yusif Abdullahi, ya fitar, an samu kiran gaggawa da misalin karfe 10:54 na dare daga wani jami’in hukumar, HFS Ibrahim Sabo, inda aka sanar da aukuwar gobarar. Nan take aka tura jami’an kashe gobara daga hedikwatar hukumar da sauran tashoshin cikin birnin Kano zuwa wurin.
Binciken farko ya nuna cewa gobarar ta samo asali ne daga kasuwar Takumbo (salvage yard), inda ta lalata kayayyaki masu yawa kafin daga bisani ta bazu zuwa bene na sama na ginin Kanawa Building, tare da lalata ofisoshi biyu, falo biyu, bandakuna biyu da kuma kicin guda. Haka kuma, ta shafi shaguna biyu da ke kasa na kamfanin TUSRAYS NIG. LTD. Hukumar ta bayyana cewa walƙiyar lantarki ce ta haddasa gobarar, tare da yin kira ga jama’a su dauki matakan kariya da kuma gaggauta kai rahoton duk wata gobara zuwa tashar kashe gobara mafi kusa.
You must be logged in to post a comment Login