Connect with us

Coronavirus

Gobe za a bude cibiyar gwajin Corona a BUK

Published

on

Cibiyar dakile cutuka masu yaduwa ta kasa NCDC ta ce a gobe Laraba sabuwar cibiyar gwajin cutar Covid-19 zata fara aiki a Kano.

Shugaban cibiyar Chikwe Ihekweazu ne ya bayyana hakan a shafinsa na Twitter, inda ya ce tuni komai ya kankama a sabuwar cibiyar gwajin cutar Corona dake jami’ar Bayero.

Ihekweazu yayi godiya ga jami’an hukumar ta NCDC da ma’aikatar lafiya ta jihar Kano da kuma asibitin koyarwa na Malam Aminu Kano.

Wannan dai na zuwa ne yayin da aiki ke cigaba da kankama a yau a Laraba a cibiyar gwajin cutar Covid-19 ta asibitin koyarwa na Malam Aminu Kano bayan shafe tsawo kwanaki a rufe sakamakon rashin kayan aiki.

Matsalar cibiyar gwajin dai ta kawo tsaiko ga aikin yaki da cutar ta Covid-19 a Kano.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!