Labarai
Gwamna Abba ya raba tallafin fiye da miliyan 55 ga masu ƙananan sana’o’i

Gwamnatin Jihar Kano ta raba tallafin kuɗi sama da Naira miliyan 55 da dubu dari takwas ga masu ƙananan sana’o’i da masu tallace-tallace a kan tituna domin bunƙasa harkokin kasuwancinsu.
Da ya ke ƙaddamar da rabon tallafin, Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya bayyana cewa mutane 1,116 ne suka amfana, inda kowanne daga cikinsu ya samu Naira dubu hamsin domin ƙarfafa sana’o’insu
Gwamna Abba ya ce, bai wa matasan tallafin kuɗi da yawan su ya zarce naira miliyan 55 lokaci guda, zai taimaka musu wajen bunƙasa sana’o’in da suke yi akan tituna da danjojin motoci a Kano tare da ɗauke hankalin su daga aikata munanan laifuka.
Gwamnan ya kuma sha alwashin ci gaba da tallafa wa masu ƙananan sana’o’i a faɗin Kano da nufin sauya tunanin matasa maza da mata a jihar daga abubuwan da basu da amfani ya zuwa yadda za su taimaka wa kansu har ma da sauran al’umma.
Wasu daga cikin matasan da aka tallafa wa sun jinjina wa yunƙurin gwamnan inda suka ba shi tabbacin cewar za su yi amfani da tallafin ta kyakkyawar hanyar musamman wadda za ta haɓɓaka tattalin arzikin Kano.
You must be logged in to post a comment Login