Connect with us

Labarai

NESREA ta fara bincike kan zargin zubewar sinadari mai hatsari a hanyar Kaduna zuwa Abuja

Published

on

Hukumar Kula da Ka’idojin Muhalli ta Tarayya, NESREA, ta fara gudanar da bincike kan wani zargin zubewar sinadari mai haɗari da ya faru a kan babbar hanyar Kaduna zuwa Abuja bayan da wata babbar mota ta yi hatsari tare da barin wani farin kumfa a wurin da lamarin ya auku.

 

A cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar, ta ce jami’anta na reshen jihar Kaduna sun ziyarci wurin domin tattara bayanai tare da ɗaukar samfurin farin kumfar, ƙasa da kuma ruwan wani rafin da ke kusa domin gudanar da gwajin kimiyya kan ainihin sinadarin da kuma tasirinsa ga muhalli.

 

Rahotannin farko sun nuna cewa hatsarin ya faru ne bayan wata babbar mota ta zubar da kayan da take ɗauke da su, lamarin da ya jawo hankalin jama’a da dama da suka riƙa tsayawa suna ɗaukar hotuna da bidiyo na abin da suka gani.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!