Labarai
Gwamna Adeleke ya sauke Sarki bayan kotun Amurka ta same shi da aikata damfara

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke, ya sauke Sarkin Ipetumodu, Oba Joseph Oloyede, bayan wata kotu a ƙasar Amurka ta same shi da laifukan damfara ta haraji da kuma halasta kudaden haram.
Matakin ya biyo bayan samun sahihin kwafin hukuncin kotun Ohio da gwamnatin ta Osun ta yi.
Mai magana da yawun gwamnan, Olawale Rasheed, ya ce, gwamnatin jihar ta Osun, ta ɗauki matakin ne domin kare martabar masarautar da tabbatar da zaman lafiya da kyakkyawan shugabanci.
Tun a watan Agustan 2025 ne kotun tarayya ta Ohio ta yankewa sarkin hukuncin daurin watanni 56 bisa laifukan damfara da kuma ƙarya wajen biyan haraji. Gwamnatin Osun ta bayyana fara shirye-shiryen naɗa sabon sarki a nan gaba kadan.
You must be logged in to post a comment Login