Labarai
Hon. Abba Anas Adamu ya rasu a hannun ‘yan bindigan da suka sace shi

Tsohon ɗan majalisar wakilai na Tarayya Hon. Abba Anas Adamu, ya rasu a hannun ‘yanbindiga bayan sace shi da suka yi kan hanyar Kaduna zuwa Abuja.
Rahotanni sun bayyana cewa a makon da ya gabata ne masu garkuwa da mutane suka sace wasu manyan ‘yan siyasa daga Jihar Jigawa, ciki har da Abba Anas Adamu, wanda ya taɓa wakiltar mazabar Birniwa/Guri/Kiri Kasama a Majalisar Tarayya kuma ya taɓa shugabantar Karamar Hukumar Guri, tare da Ali Tukur Gantsa, tsohon Sakataren Jam’iyyar PDP na Jihar kuma jigo a Jam’iyyar ADC a jihar, yayin da suke kan hanyar Kaduna zuwa Abuja.
Sanata Sabo Mohammed Nakudu CON daga Jihar Jigawa ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana ta’aziyyarsa a shafinsa na Facebook.
Rahotonni sun tabbatar cewa Hon. Abba Anas Adamu ya rasu a hannun masu garkuwar, Za’a gundanar da Jana’izar Marigayi Hon. Abba Anas Adamu a yau Talata, a gidansa da ke Zangon Dakata bayan Ofishin hukumar WAEC da ke kan Titin Dakata zuwa Bela, da Karfe 10:00 na safe.
Yayin da kuma aka samu labarin kubutar Ali Tukur Gantsa daga hannun masu garkuwar.
You must be logged in to post a comment Login