Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamna Ganduje na jagorantar kwamitin binciken rikicin siyasar jihar Edo

Published

on

Gwamna Abdullahi Umar Ganduje na jagoranta kwamitin na mutane biyar karkashin jami’yyar APC dangane da rikicin da ke afkuwa a jam’iyyar ta APC a jihar Edo.

Sakataren jamiyyar ta kasa Lanre Issa-Onilu ne ya bayyana haka a yayin da yake amsa tambayoyin ‘yan jarida.

idan za’a iya tunawa dai jamiyyar APC ta kasa ta kafa kwamitin da zai binciki matsalar da ke faruwa a jam’iyyar reshen jihar Edo wanda gwamna Abdullahi Ganduje ke jagoranta.

Mambobin da ke cikin kwamitin dai akwai gwamnan jihar Katsina , Aminu Masari da tsohon gwamna Oyo Abiola Ajimobi da tsohon gwamnan jihar Borno sannan sanata Kashim Shettima da Ahmad Wadada wanda shine sakataren kwamitin.

Tuni dai ‘yan jam’iyyar suka fara damuwa kan jan kafa da kwamitin yake wajen bayyana sakamakon rahoton sa.

Ya kara da cewa tuni aka basu ka’idojin da zasu yi amfani da shi wajen gudanar da binciki , a don haka ne aka zabi wadanda ke cikin kwamitin don samun sakamakon da ya dace.

Yau Ganduje da Abba kowa zai san matasayin sa-Kotun daukaka kara

Ganduje ya rantsar da kwamishinoni ranar tantancewa

Ganduje ya sabunta yarjejeniyar tallafin karatun Digiri na biyu da kasar Faransa

Sakataren jamiyyar ya ce ba zasu iya tantancewa ko kwamitin ya fara aiki ba tare da sun bayyana sakamakon ba.

Akwai dai rashin jituwa da ke faruwa tsakanin gwamna Godwin Obaseki da  shugaban jamiyyar Adams Oshiomole, a halin yanzu

Kwanankin baya ne dai shugaban jamiyyar ta APC ya zargin gwamna Edo da aiko da ‘yan bangar siyasa a filin da ake taron yaye dalibai dake Edo domin su tozarta shi.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!