Labarai
Gwamna Makinde ya yaba wa Shugaba Tinubu bisa nasarar ceto ɗalibai da malaman jihar

Gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde, ya miƙa godiyarsa ga Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, da jami’an tsaron Najeriya bisa nasarar ceto ɗalibai da malamai da aka yi garkuwa da su a jihar.
Makinde ya bayyana hakan ne a yayin shirin Politics Today na tashar Channels Tv a ranar Juma’a,
Gwamnan ya ce gwamnatin jihar na amfani da wannan dama wajen nuna godiya ga dukkan jami’an tsaro da kuma Shugaba Tinubu saboda ƙoƙarin da suka yi domin tabbatar da nasarar aikin ceton.
Kalaman Makinde na zuwa ne bayan jami’an tsaro sun ceto ɗalibai da malamai da aka yi garkuwa da su, bayan sun shafe kwanaki 56 a hannun masu garkuwa da mutane.
You must be logged in to post a comment Login