Connect with us

Labarai

Gwamnatin Jigawa ta kashe fiye da biliyan 300 wajen gina hanyoyi da wasu ayyuka

Published

on

Gwamnatin jihar Jigawa ta kashe sama da Naira biliyan 300 wajen ginin hanyoyi da sauran ayyukan more rayuwa cikin shekaru 2.

 

Babban daraktan hukumar tabbatar da bin ka’idojin Kwangila da bibiyar aiyuka Kasim  Muhammad ne ya bayyana a gurin rufe wani taro da aka gudanar a garin Gumel.

 

A cewar daraktan gwamnatin jihar ta bada Kwangilar sabin hanyoyi 46 wadda ya kai kilomita 976 a shekarar da ta gabata, tare da karasa aiyukan da aka gada daga gwamnatin baya.

 

Haka nan ya kara da cewa saukaka zirga-zirga da bunkasa noma da safarar kayayyaki daga wani bangaren zuwa wani ma daga cikin manufar yin aiyukan.

 

Kazalika ya ce gwamnatin jihar karkashin jagorancin gwamna Malam Umar Namadi ta bayar da wasu aiyukan masu yawa a bangaren Lafiya da Ilimi da kuma Noma don inganta rayuwa da kuma walwalar al’ummar jihar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!