Labarai
Gwamnatin Tarayya na shirin sake ciyo sabon bashin sama da Dala biliyan 1 a Bankin duniya

Gwamnatin Tarayya ta fara tattaunawa da Bankin Duniya don karbar sabon bashin kudi na sama da Dala biliyan 1.
Sabon bashin a cewar gwamnatin za a zuba shi a fannonin sauye-sauyen tattalin arziki, samar da ayyukan yi da sauran su.
Rahotanni sun tabbatar da cewa idan har aka ciyo wannan bashi, zai zama bashi na biyu mafi girma da gwamnatin Nijeriya karkashin shugaba Tinubu ta ciyo, bayan wanda ta karba a watan Yunin 2024 na Dala biliyan 1 da Miliyan Dari Biyar.
You must be logged in to post a comment Login