Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnatin Kano ta bada Umarnin a kama duk wanda yaki karbar tsahon kudi yayin cinikayya

Published

on

Gwamnatin Kano ta ce zata rufe wurin sana’ar duk wanda ya ƙi karɓar tsohon kuɗi a hannun jama’a.

Shugaban Hukumar kula da Zirga-zirga Ababen Hawa ta jihar Kano KAROTA Baffa Babba Dan’agundi ne ya bayyana haka a yau.

Baffa Babba ‘Dan’agundi ya ce, Gwamna Dr. Abdullahi Umar Ganduje ne ya bayar da umurnin rufe duk wani gurin kasuwance a faɗin jihar nan da yaƙi karbar tsofaffin kuɗin.

Baffa Babba ya ce ”an ɗauki matakin ne saboda ƙorafe-korafen jama’a da ya yi yawa na ƙin karɓar tsofaffin kuɗin a hannun jama’a, musamman a wasu daga cikin gidajen mai da Asibitoci da wajen saye da sayarwa na faɗin jihar nan.”

Hakan ya biyo bayan umarnin da babban bankin ƙasa CBN ya bayar na ci gaba da karbar tsofaffin kuɗin.

Tuni dai Gwamnan ya bayar da umurni ga Kwamitin Kar-ta-kwana mai kula da gidaje Mai su fita su tabbatar ana karɓar tsofaffin kuɗin.

Ya bayyana cewa duk wanda yaƙi bin umarnin ya saɓa da dokar Hukumar kula da Haƙƙin mai saye da sayarwa ta Consumer Protection Council, sashe na 10 ƙaramin sashi na 1(b) da kuma sashe na 10 ƙaramin sashi na 2 na dokar Hukumar

Ya ƙara da cewa ”duk wanda aka kama za a rufe wajen kasuwancinsa tare da gurfanar da shi a gaban Shari’a domin daukar mataki na gaba”.

Labari: Abba Isa

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!