Connect with us

Labarai

Gwamnatin Kano ta haɗa kai da manyan makarantu wajen dashen bishiyoyi

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano ta haɗa kai da manyan makarantun gaba da sakandare wajen faɗaɗa shirin dashen bishiyoyi da kare muhalli.

 

Kwamishinan Albarkatun Ruwa, Muhalli da Sauyin Yanayi, Dakta Dahiru Muhammad Hashim, ya ƙaddamar da shirin a Kwalejin Musulunci da Ilimin Shari’a ta Mallam Aminu Kano, wato Legal.

 

Ya ce gwamnatin jihar na shirin dasa bishiyoyi miliyan goma a bana, bayan shirye-shiryen dasa miliyan ɗaya da miliyan uku da ta aiwatar a baya.

 

Ya ce bishiyoyi na taimakawa wajen tsaftace iska, rage zafin yanayi da yaƙi da zaizayar ƙasa.

 

A nata ɓangaren, makarantar ta nemi tallafin gwamnati wajen samar da ruwa, greenhouse da magungunan yaƙi da ƙwari da cututtukan amfanin gona.

 

Kwamishinan ya bayar da umarnin a haƙa wa makarantar rijiyar burtsatse, tare da cewa gwamnati na ci gaba da ƙoƙarin inganta samar da ruwa a jihar.

 

An kammala taron da dashen bishiyoyi tare da ɗalibai da mahukuntan makarantar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!