Connect with us

Labarai

Dakarun sojin kasar nan sun hallaka yan ta’adda 60

Published

on

Rundunar Sojin kasar nan, ta ce dakarunta sun hallaka ’yan ta’adda sittin da biyar tare da kubutar da mutane talatin da hudu da aka yi garkuwa da su, yayin wasu ayyukan da suka gudanar a sassan kasar cikin makon da ya gabata.

 

Daraktan yada labaran ayyukan tsaro na rundunar, Manjo Janar Michael Onoja, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar aka rabawa manema labarai.

 

Ya ce ayyukan sun gudana ne daga ranar 7 zuwa 13 ga watan Agustan 2026, inda dakarun suka ci gaba da kai farmaki kan maboyar ’yan ta’adda da kuma kokarin ceto mutanen da aka yi garkuwa da su.

 

Rundunar ta ce za ta ci gaba da ayyukan soji domin dakile ayyukan ta’addanci da sauran laifukan da ke barazana ga tsaron al’umma.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!