Labarai
kungiyoyin NASU da SSANU za su katse yajin aiki

Kwamitin Hadin Gwiwa na ma’aikatan Jami’a JAC, ya ce hadakar kungiyoyin manyan ma’aiktan jami’o’in Najeriya za su dakatar da yajin aiki ranar litinin mai zuwa.
Hakan na cikin sanarwar hadin gwiwa da babban sakataren kungiyar NASU da kuma shugaban SSANU Muhammad Ibrahim suka fitar a Abuja.
Sanarwar ta ce janye yajin aikin ya biyo cimma matsaya da kungiyar ta yi da gwamnati kan biyan bukatun mambobinsu.
You must be logged in to post a comment Login