Connect with us

Labarai

Gwamnatin Kano za ta tilastawa kamfanoni masu zaman kansu bai wa al’ummar jihar ayyukan yi

Published

on

Kwamitin tabbatar da daidaito na rabon guraben aiki ga al’ummar jihar Kano ya ce nan gaba kadan dokar da za ta tilastawa kamfanoni masu zaman kansu bawa al’ummar jihar nan guraben aiki za ta fara aiki.

Shugaban kwamitin  Dakta Ibrahim Garba Muhammad ne ya bayyana halin da ake ciki kan aikin da kwamitin ya sanya a gaba.

Yace yanzu haka ana kokari a fito da wani jadawali wanda zai tabbatar da cewa dukkanin wata ma’aikata da za ta shigo jihar Kano ta gudanar da kasuwanci dole ne ta bada gurbin aiki ga al’ummar Kano.

Dakta Ibrahim Garba Muhammad nan bada jimawa ba za’a fito da dokar kuma  za ta fara aiki a dukkanin ma’ikatu da kamfanoni masu zaman kansu. 

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!