Labarai
Gwamnatin Najeriya da Amurka na shirin ƙulla yarjejeniya kan hakar ma’adinai

Gwamnatin Najeriya da kasar Amurka na shirin ƙulla yarjejeniyar fahimtar juna, ta MOU, domin ƙarfafa haɗin gwiwa a fannin hakar ma’adinai.
Ministan Ma’adanai na Najeriya, Dele Alake, ya ce haɗin gwiwar zai mayar da hankali kan binciken ma’adinai, haƙa, sarrafawa da tace su, tare da jawo hankalin masu zuba jari na ƙasashen waje.
Ya ce Najeriya na da dimbin ma’adinai kamar zinare a Zamfara da lithium a jihohin Nasarawa, Kebbi da Taraba. Ministan ya kuma ce manyan kamfanonin hakar ma’adinai na duniya, ciki har da Fortescue, Glencore da BHP, na nuna sha’awar zuba jari a Najeriya.
You must be logged in to post a comment Login