Labarai
Gwamnatin Tarayya na shirin gyara wuraren kiwon dabbobi guda 417

Gwamnatin Tarayya, ta ce, za ta gyara wuraren kiwon dabbobi guda 417 tare da samar da matsugunan kiwon dabbobi na zamani a yankuna shida da ake yawan samun rikicin manoma da makiyaya.
Ministan ma’aikatar kula da harkokin kiwo, Malam Idi Mukhtar Maiha, ya ce, jihohin Benue da Filato da Nasarawa da Kaduna da Adamawa da kuma birnin tarayya Abuja ne aka fi bai wa fifiko a cikin tsarin.
Haka kuma, ya ce, gwamnati ta fara aiwatar da gwaji jihar a Filato domin sauya tsarin kiwon dabbobi daga yawo zuwa kiwon dabbobi a wuraren da aka tanada don magance matsaloli.
You must be logged in to post a comment Login