Labarai
Gwamnatin Tarayya ta ayyana Talata 25 ga Agusta 2026 a matsayin ranar hutun bikin Mauludi

Gwamnatin Tarayya ta ayyana Talata, 25 ga watan Agusta, 2026, a matsayin ranar hutun bikin Mauludi, don tunawa da zagayowar ranar haihuwar Annabi Muhammad ﷺ.
Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo, ne ya sanar da hakan a madadin gwamnatin tarayya, cikin wata sanarwa da Babbar Sakatariyar ma’aikatar, Dakta Magdalene Ajani, ta fitar a yau Juma’a.
Ministan ya taya Musulmin kasar nan da sauran sassan duniya murnar wannan rana, tare da kira gare su da su yi tunani kan darussan tausayi, tawali’u da kuma hidima ga al’umma, wadanda suka kasance daga cikin kyawawan halayen rayuwar Annabi Muhammad ﷺ.
Ya ce wadannan dabi’u na daga cikin abubuwan da kasar nan ke matukar bukata a halin da take ciki, inda ya bukaci kowa da kowa, ba Musulmi kadai ba, da ya yi tunani a kansu.
Ministan ya kuma bukaci mutane da su yi amfani da wannan lokaci wajen yin addu’ar samun zaman lafiya da hadin kan kasa, yana mai cewa tabbatar da zaman lafiya da hadin kai nauyi ne da ya rataya a wuyan kowa.
You must be logged in to post a comment Login