Labarai
Gwamnatin tarayya ta sanar da ranakun hutun Sallah

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Laraba 27 da Alhamis 28 ga watan Mayun 2026 a matsayin ranakun hutun bikin Babbar Sallah.
Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo, ya bayyana a matsayin girmamawa ga Musulman kasar nan da ma sauran al’ummar Musulmi na duniya.
Ya kuma bukaci ‘yan kasar nan su yi amfani da lokacin wajen addu’a domin zaman lafiya da tsaro da ci gaban ƙasa tare da ƙarfafa haɗin kai da zaman tare lafiya.
You must be logged in to post a comment Login