Connect with us

Labarai

Gwamnonin Arewa sun kafa Asusun Tsaro tare da rantsar da kwamitin amintattu

Published

on

Gwamnonin jihohin Arewa sun kafa Asusun Tsaron Arewacin Najeriya, tare da rantsar da kwamitin amintattu da zai kula da tafiyar da asusun.

Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Arewa, Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya ce an ɗauki matakin ne domin ƙarfafa haɗin gwiwa da hukumomin tsaro wajen yaƙi da matsalolin ‘yan bindiga, ta’addanci, garkuwa da mutane da sauran laifuffuka.

Ya ce asusun zai taimaka wajen tattara kuɗaɗe, inganta musayar bayanan sirri da kuma tallafa wa ƙoƙarin hukumomin tsaro na kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Haka kuma ya jaddada cewa dole ne a magance tushen matsalolin rashin tsaro da suka haɗa da talauci, jahilci, rashin aikin yi da kuma yawan yaran da ba sa zuwa makaranta.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!