Labarai
Shugaba Mnangagwa ya tsawaita mulkinsa da karin shekaru 2

Shugaban ƙasar Zimbabwe, Emmerson Mnangagwa, ya tsawaita wa’adin mulkinsa da karin shekaru 2, lamarin da zai ba shi damar ci gaba da zama shugaban ƙasar har zuwa shekarar 2030.
Baya ga tsawaita wa’adin mulkinsa, an kuma sauya tsarin zaɓen shugaban ƙasa inda aka soke damar da ’yan ƙasa ke da ita ta zaɓen shugaban ƙasa kai tsaye.
A karkashin sabon tsarin, ‘yan majalisar dokokin ƙasar ne za su riƙa zaɓen shugaban ƙasa maimakon kuri’ar kai tsaye daga al’umma.
Haka kuma, an ƙara tsawon wa’adin shugaban ƙasa daga shekara 5 zuwa shekara 5, a wani gagarumin sauyi da ya shafi tsarin mulkin ƙasar Zimbabwe.
You must be logged in to post a comment Login