Labarai
Mazauna Dorayi sun nemi daukin mahukunta kan matsalar ambaliya

Mazauna unguwar Dorayi bayan gidan Sarkin Dutse sun koka kan matsalar ambaliyar Ruwa a a yankin, tare da neman daukin mahukunta.
Hakan na cikin wata sanarwa da kungiyar gamayyar gazauna mazauna yankin suka fitar mai dauke da sa hannun Dakta Yusif Ibrahim.
Sanarwar ta ce sama da shekaru ashirin matsalar ke haifar musu da matsananciyar ambaliyar ruwa idan anyi ruwan Sama, sakamakon ƙarancin magudanar ruwa a yankin.
A cewar su matsalar ta haddasa musu asarar rayuka da dukiyoyi hadi da lalacewar gidaje da hanyoyi, tare da jefa al’umma cikin mawuyacin hali.
A sabo da haka ne ta cikin sanarwar suke, kira ga Gwamnatin Kano da shugabannin yankin na Dorayi da hukumar REMASAB da sauran hukumomi kan su kai musu dauki.
You must be logged in to post a comment Login