Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Hakkin miji ne ya bai wa matarsa cikakkiyar tarbiyya bayan aure – Farfesa

Published

on

Kwamitin bibiyar al’amuran da suka shafi auratayya ta Jihar Kano ya ce hakkin miji ne ya bai wa matarsa cikakkiyar tarbiyya bayan aure.

Sakataren kwamitin Farfesa Usman Zunnuraini ne ya bayyana hakan a yau ta cikin shirin Barka da Hantsi na nan tashar Freedom, wanda ya maida hankali kan hanyoyin da za a bi don rage yawaitar mace-macen aure.

Ferfesa Usman Zunnurainin ya kara da cewa, kamata ya yi kowacce mace tasan hakkin mijinta kuma shi ma miji yasan hakkinsa, da nufin kawo zaman lafiya a tsakaninsu.

Yana mai cewa, rashin tsafta da rashin adana dukiyar miji na kawo raguwar soyayya tsakanin ma’aurata, a cewa sa, babu wani dalili da zai sa miji ya boye wa matarsa karin auren saboda wani dalili na kashin kansa.

Farfesa Zunnuraini ya kuma yi kira ga ma’aurata da su kasance masu biyayya da aure kamar yadda addinin musulunci ya tanada.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!