Connect with us

Labarai

Jihar Kaduna ta kammala jigilar Alhazan ta daga Madina zuwa Makkah

Published

on

Hukumar jin dadin Alhazan jihar Kaduna ta bayyana cewa ta kammala jigilar dukkanin Alhazan jihar daga Madina zuwa Makkah a jiya Juma’a domin ci gaba da gudanar da aikin Hajjin bana.

 

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar Kaduna, Ibraheem Musa, ya fitar, an ce an samu nasarar jigilar Alhazan cikin sauki ne sakamakon shiri tun da wuri da kuma goyon bayan gwamnatin jihar ga aikin Hajjin 2026.

 

Daraktan ayyuka na hukumar Alhazai ta jihar Kaduna, Abubakar Yusuf, ya ce Alhazan sun kwashe kwanaki hudu na wajibi a Madina kafin a fara jigilar su zuwa Makkah rukuni-rukuni, inda rukuni na karshe zai tashi a yau Juma’a.

 

Ya kara da cewa tun kafin fara aikin Hajji aka rika gudanar da shirye-shiryen wayar da kan maniyyata a fadin jihar, domin ilmantar da su kan dokokin Saudiyya da yadda za su gudanar da kansu yayin ibadar Hajji.

 

Hukumar ta kuma bayyana cewa tawagar Hajjin jihar Kaduna tare da jami’an hukumar sun ziyarci wani Alhaji mai suna Sani Garba wanda aka kwantar a asibitin Almiqati da ke Madina, inda daga bisani aka sallame shi sannan aka wuce da shi zuwa Makkah ranar Alhamis.

 

An kuma bayyana cewa an sauke Alhazan Kaduna ne a unguwar Misfalah da ke Makkah, kusa da titin Ibrahim Khalil, wanda ke da nisan tafiya kadan zuwa Masallacin Harami.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!