Connect with us

Labarai

Gwamnatin Kwara ta sanar da ranar fara jigilar maniyyata Hajjin bana

Published

on

Gwamnatin Jihar Kwara ta sanar da cewa za a fara jigilar maniyyatan aikin Hajjin shekarar 2026 daga ranar 6 ga watan Mayu mai kamawa. 

 

Hukumar kula da aikin Hajji ta jihar ta bayyana cewa an kammala shirye-shiryen da suka haɗa da tsara jadawalin tashi, da kuma raba sabbin katinan shaida ga maniyyatan domin saukaka tantancewa da tsaro.

 

Haka kuma, an bukaci dukkan maniyyata su kammala duk wasu muhimman abubuwa kamar allurar rigakafi, tantance takardu, da halartar bitar horo kafin ranar tashi.

 

Jihar ta tabbatar da cewa za a gudanar da aikin cikin tsari da aminci domin tabbatar da jin daɗin maniyyata yayin gudanar da ibadar Hajjin bana.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!