Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

IGD2020: Citad ta nemi gwamnatoci su bai wa haƙƙin mata muhimmanci

Published

on

A yayin da ake bikin ranar ‘ya’ya mata ta duniya a yau, cibiyar bunkasa fasahar sadarwar zamani CITAD ta bukaci gwamnatocin Najeriya da su kara bai wa dokar hakkin ‘ya’ya mata muhimmanci.

Babbar jami’ar shirye-shirye ta cibiyar Maryam Ado Haruna ce ta bayyana hakan ta cikin sanarwar da ta fitar.
Sanarwar ta ce kamata yayi gwamnatoci su mayar da hankali wajen yaki da cin zarafin ‘ya’ya mata musamman ma ta bangaren yi musu gyade.

Maryam Ado Haruna ta cikin sanarwar ta bukaci da a samar da wani tsari da zai rika samarwa ‘ya’ya mata ayyukan dogaro da kan su da kuma tsame su daga kangin talauci da sauran ayyukan cin zarafi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!