Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

ilimi

Ilimi: Za mu tallafawa makarantun islamiyya da tsangayu a Kano – Ɗan-Zarga

Published

on

Hukumar kula da makarantun islamiyya da na tsangaya a jihar Kano ta yi kira ga al’umma da su riƙa talafawa makarantun.

Hukumar ta buƙaci hakan musamman daga ɓangaren don bunƙasa ilimin addinin musulunci.

Shugaban hukumar Gwani Yahuza Ɗan-Zarga ne ya yi wannan kira jim kaɗan bayan kammala taron masu ruwa da tsaki da gidauniyar Khalifa Dankade ta shirya da haɗin gwiwar ofishin jakadancin Amurka a nan Kano.

“Da ma can abu ne da ya kamata ayi tun da daɗewa kuma munata kiraye kiraye ga ƙungiyoyin mu da su ɗauki gabarar yin wannan tsarin dan tallafawa makarantun mu na addini da kuma islamiyya duba da cewa suma suna buƙatar tallafi”.

Maƙa sudin taron dai shi ne tattaro dukkanin masu ruwa da tsaki don tattaunawa tare da samo mafita kan sha’anin ilimin addini.

Gidauniyar za ta tallafawa tsangayu sittin a jihohi shida na arewacin Ƙasar nan a matsayin gwaji, har na tsawon shekara guda.

 

 

 

 

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!