Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Covid-19: Gwamnatin Kano ta bada umarnin rufe makarantun Allo dana Islamiyya

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta bada umarnin rufe dukkan Tsangayun karatun alkur’ani da makarantun Islamiyya dake fadin jihar don kaucewa annobar Coronavirus.

Shugaban hukumar Tsangayu da makarantun allo ta jihar Kano Gwani Yahuza Dan Zarga ne ya bayyana hakan kamar yadda jaridar Solacebase ta rawaito.

Gwani Dan Zarga ya ce za a rufe makarantun daga ranar Litinin 23 ga watan Maris da muke ciki, kuma hakan ya biyo bayan cimma matsayar da gwamnonin arewa maso yammacin kasar nan su kayi ta rufe dukkan makarantu a yankin.

Idan baku manta ba, a ranar Alhamis ne gwamnonin jihohin Arewa maso yammacin kasar nan suka amince a rufe makarantun yankin domin takaita cudanyar jama’a da dama, wanda hakan ka iya taka rawa wajen yaduwar cutar Coronavirus.

Karin labarai:

Covid-19: An fara rufe makarantun Islamiyya a Kano

Covid-19: An dakatar da kwallon kafa a Kano saboda Coronavirus

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!