Labarai
Immigration ta ce sabon tsarin buga Fasfo bai shafi rajista a jihohi ba

Hukumar Kula da Shige da Fice ta kasa ta ce sabon tsarin da ta bullo da shi na buga fasfo a Abuja bai shafi yin rijista ko karɓar fasfo a jihohin ƙasar ba.
Hukumar ta bayyana cewa rahotannin da ke cewa an cire cibiyoyin gudanar da fasfo daga Kano ba gaskiya ba ne, illa dai mutane sun yi kuskuren fahimtar sabon tsarin.
Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar a Kano, DSI Muhammad Auwal, ya ce sabon tsarin ya fara aiki tun farkon shekarar nan, inda aka fara aiwatar da shi a jihohi daban-daban.
Ya ce abin da aka mayar zuwa Abuja shi ne buga fasfo kawai, amma har yanzu ana ci gaba da yin rijista da kuma karɓar fasfo a dukkan cibiyoyin da ke jihohi, ciki har da nan Kano.
DSI Auwal ya kuma tabbatar da cewa takardar da ake yaɗawa a kafafen sada zumunta ta fito ne daga hukumar, sai dai ya ce takarda ce ta cikin gida wadda ba a yi niyyar ta fito bainar jama’a ba.
A cewarsa, manufar mayar da buga fasfo wuri guda ita ce ƙarfafa tsaro, da rage yiwuwar buga fasfo na bogi.
Ya kuma ƙara da cewa jihar Legas tana cikin rukuni na gaba da za a aiwatar da sabon tsarin nan ba da jimawa ba.
You must be logged in to post a comment Login