Connect with us

Labarai

Atiku ya koka kan tura kudi asusun sa ba tare da sanin sa ba

Published

on

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar ADC, Atiku Abubakar, ya bayyana damuwa bayan an tura kuɗi zuwa asusun ajiyarsa na sirri ba tare da saninsa ko amincewarsa ba.

 

A cikin wata sanarwa da mai taimaka masa kan yaɗa labarai, Phrank Shaibu, ya fitar, Atiku ya ce mutumin da ya tura kuɗin ba a san shi ba, kuma ya rubuta “Contribution Electioneering Campaign,” ma’ana “Gudunmawar Kamfen ɗin Zaɓe.”

 

Atiku ya ce shi da tawagarsa ba su nemi ko amince da irin wannan gudunmawa ba, yana mai cewa abin da ya fi tayar da hankali shi ne yadda aka samu bayanan asusun nasa na sirri, duk da cewa ba a bayyana su ga jama’a ba.

 

Ya ce idan har bayanan asusun sirrin tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa za su iya shiga hannun wasu ba tare da izini ba, hakan na nuna cewa sirrin bayanan kuɗin kowane ɗan kasa na cikin haɗari.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!