Connect with us

Labarai

Dole EFCC da DSS su faɗaɗa bincike kan zargin kafa hukumar bogi – Temitope Ajayi

Published

on

Ɗaya daga cikin hadiman Shugaba Bola Tinubu, Temitope Ajayi, ya yi kira ga Hukumar EFCC da DSS da kuma Rundunar Ƴansanda su faɗaɗa bincike kan zargin kafa wata hukumar bogi, tare da gano waɗanda suka taimaka wa wanda ke ikirarin shugabantar hukumar Adeyemi Adeniyi Matthew. 

A cewarsa, akwai yiwuwar wasu daga cikin jami’an gwamnati sun taka rawa a lamarin, kuma suna ƙoƙarin jefa zargi kan shugaban ma’aikatan fadar shugaban ƙasa, Femi Gbajabiamila.

Lamarin ya biyo bayan iƙirarin da Prince Adeniyi Adeyemi ya yi cewa Shugaba Tinubu ya naɗa shi shugaban wata hukuma mai suna Kwamitin Shugaban Ƙasa kan Shawarwarin Tattalin Arziki. 

Sai dai Fadar Shugaban Ƙasa ta bakin Femi Gbajabiamila da mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, sun musanta hakan, tare da cewa gwamnatin tarayya ba ta da irin wannan hukuma.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!