Labarai
INEC ta sanar da ranar yin zabukan cike gurbi na kujerun majalisar tarayya
Hukumar zabe mai zaman kanta ta Najeriya INEC ta sanar da ranar Asabar, 20 ga Yunin 2026 domin gudanar da zabukan cike gurbi na kujerun majalisu da suka zama babu kowa a kai a jihohi shida da suka hada da Kebbi da Kano da Ondo da Rivers sai Nasarawa da kuma Enugu.
A cewar hukumar, kujerun Sanatoci guda hudu ne za a cike, kana za a gudanar da zaben cike gurbi na kujera guda daya ta Majalisar Wakilai a Jihar Kano, da kuma kujera guda daya ta Majalisar Dokokin Jihar Kebbi.
INEC ta bayyana cewa za a gudanar da wadannan zabuka ne a rana guda da zaben gwamnan Jihar Ekiti da aka shirya yi a ranar 20 ga Yuni, 2026.
Shugaban INEC, Farfesa Joash Amupitan, ne ya bayyana jadawalin zaben yayin rantsar da sabuwar Kwamishinar Kasa, Rear Admiral Jamila Malafa mai ritaya.

You must be logged in to post a comment Login