Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Inganta tsaro a filayen wasanni zai kawo karshen shaye-shaye a Kano – Dagaci

Published

on

Dagacin Sharada Alhaji Ilyasu Mu’azu ya shawarci gwamnati kan ta kara yawan ma’aikata dake kula da filin wasanni na kofar Na’isa don samar da tsaro da kawo karshen matsalar sayar da miyagun kwayoyi musamman a unguwannin dake makotaka da filin.

Alhaji Ilyasu Mu’az ya bayyana hakan ne lokacin da yake zantawa da manema labarai, yana mai cewa sun dauki matakin ganawa da masu irin wannan sana’ar ta sayar da kwayoyi a unguwar domin nema musu makoma ta hanyar basu jari don su dogara da kansu.

Dagacin na unguwar Sharada ya kara da cewa suna sake kira ga masu gudanar da sana’ar sayar da kayan maye ga ‘ya’yan jama’a da su sake tunani su kuma dawo domin a nema musu makoma domin su tsira a wajen haliccinsu kasancewar suna cutar da al’umma.

Rubutu masu alaka : 

Da mu za’a kawo karshen shaye-shayen miyagun kwayoyi –ALGON

Gwamnatin Kano za ta kafa hukumar yaki da shaye-shayen kayan maye

Wakilin mu Abdulkarim Muhammad Tukuntawa ya ruwaito dagacin na unguwar sharada Alhaji Ilyasu na shawartar jami’an tsaro da suji tsoran Allah a cikin ayyukansu musamman wajen ganin an hukunta duk wanda aka kama da aikata laifi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!