Connect with us

Ƙetare

Iran ta ce har yanzu ba su fitar da matsaya kan yarjejeniya da Amurka ba

Published

on

Iran ta jaddada cewa har yanzu ba ta kai ga yanke hukunci na ƙarshe ba akan yarjejeniyar kawo ƙarshen yaƙin da Amurka ke yi da ita, duk da cewa Shugaba Trump ya sake nanata cewa akwai yiwuwar nan bada jimawa ba za a sanya hannu akan yarjejeniyar.

Da yake jawabi ga dandazon magoya bayansa ta bidiyo a daren ranar Alhamis, Mista Trump ya shaida wa taron cewa: “A yau mun kawo ƙarshen yaƙin da muke da Iran.”

Da dama daga irin waɗannan iƙirarin a baya na cewa yaƙin na gab da ƙarewa ba su tabbata ba, sai dai sabbin kalaman shugaban sun sake ƙarfafa kasuwannin hannayen jari, tare da jawo farashin mai ya sauka.

Ma’aikatar harkokin wajen Iran ta ce a halin yanzu tana nazarin ƙunshin yarjejeniyar da aka gabatar mata, amma Tehran ba za ta yi sassauci kan mahimman sharuɗɗanta ba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!