Ƙetare
An amince da tsagaita wuta a Labanon bayan hare-haren Isra’ila

Isra’ila da ƙungiyar Hezbollah sun amince da tsagaita wuta a Lebanon bayan wani harin da aka kai cikin dare wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane aƙalla 47, a cewar ma’aikatar lafiya.
Isra’ila ta ce hare-haren na mayar da martani kan ayyukan ƙungiyar Hezbolah, ciki har da wani harin da aka kai cikin dare wanda ya yi sanadiyar mutuwar sojojin Isra’ila huɗu.
Tsagaita wutar ta fara aiki ne da ƙarfe 16:00 agogon ƙasar amma ƴan wakilan mu da ke ƙasa sun ce anci a gaba da kai hare-hare.
Wannan dai wani gwaji ne na yarjejeniyar da Amurka da Iran suka ƙulla a farkon wannan makon, wadda ta buƙaci a dakatar ayyukan soji a dukkan fagen daga da suka haɗa da Lebanon.
Rundunar IDF dai ta sha alwashin “ci gaba da kawar da duk wata barazana nan take” da kuma “mai da martani kan duk wani abu da Hezbollah ta aikata”.
A halin da ake ciki, ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya ce duk wani saɓa alƙawari da Isra’ila ta yi “za a rataya wa Amurka alhakinsa”.
You must be logged in to post a comment Login