Connect with us

Ƙetare

Iran za ta gudanar da jana’izar kwanaki uku ga tsohon Jagoran Addini Khamenei

Published

on

Mahukuntan Iran sun sanar da cewa za su gudanar da jana’izar ƙasa ta kwanaki uku ga tsohon Jagoran Addinin ƙasar, Ali Khamenei, wanda aka ce ya rasu sakamakon hare-haren haɗin gwiwar Amurka da Isra’ila a ranar farko ta yaƙin Gabas ta Tsakiya.

 

Rahotanni sun ce Khamenei, wanda ya jagoranci Jamhuriyar Musulunci ta Iran na kusan shekara 37, ya mutu a gidansa da ke tsakiyar birnin Tehran a ranar 28 ga Fabrairu, 2026. An shirya gudanar da jana’izarsa tun ranar 4 ga Maris, amma aka ɗage ta saboda yaƙin da ya ɓarke a yankin.

 

Mataimakin magajin garin Tehran, Mohammad Amin Tavakolizadeh, ya bayyana cewa za a gudanar da jana’izar jama’a na tsawon kwanaki uku, kuma ana sa ran za ta gudana a farkon watan Muharram. Ya ce za a yi bukukuwan jana’izar a Tehran da kuma biranen addini na Qom da Mashhad, inda za a binne Khamenei.

 

Tavakolizadeh ya ƙara da cewa ana sa ran mutane har miliyan 20 za su halarci jana’izar, yayin da bikin da za a yi a Tehran kaɗai zai ɗauki aƙalla sa’o’i 24.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!