Labarai
Isra’ila ta cigaba da kai hari a Lebanon

Sojojin Isra’ila sun ci gaba da rusa gidaje a garin Bint Jbeil da ke kudancin ƙasar Lebanon, a cewar kafar yada labaran gwamnatin ƙasar.
Rahoton ya ce ana sake tayar da bama-bamai domin rusa gidaje a garin, wanda ke kusa da iyakar Israel, kimanin kilomita biyar.
Garin na Bint Jbeil ya kasance wurin da aka gwabza kazamin fada tsakanin sojojin Isra’ila da kungiyar Hezbollah kafin yarjejeniyar tsagaita wuta ta kwanaki 10 da aka fara aiwatarwa a ranar Alhamis.
Wannan gari yana da muhimmanci a rikicin, domin a nan ne aka yi manyan faɗace-faɗace tun lokacin yaƙin shekara ta 2006.
A baya, ministan tsaron Isra’ila Israel Katz ya bayyana cewa rusa gidajen na daga cikin matakan da ake ɗauka domin kawar da barazanar tsaro a yankin kan iyaka.
Sai dai ministan tsaron Lebanon Michel Menassa ya soki wannan mataki, yana mai cewa hakan na iya janyo tilastawa dubban mutane barin gidajensu tare da lalata kauyuka gaba ɗaya.
You must be logged in to post a comment Login