Labarai
SSANU ta bayyana shirin ta na tsunduma yajin aiki na sai baba ta gani

Kungiyar manyan ma’aikatan jami’o’i ta kasa SSANU ta bayyana shirin ta na shiga yajin aikin sai baba ta gani, yayin da wa’adin ranar 30 ga watan Afrilu na kammala sabunta yarjejeniya da gwamnatin tarayya ke karatowa.
Kungiyar ta ce har yanzu ba a cimma matsaya ba a tattaunawar da ake yi da gwamnati, lamarin da ke barazana ga ci gaba da ayyukan jami’o’i a faɗin kasar nan.
SSANU ta ce idan aka kai ranar ba tare da samun cikakkiyar matsaya ba, ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen fara yajin aikin domin neman hakkokin mambobinta.
Haka kuma ta bukaci gwamnati da ta gaggauta daukar matakan da suka dace domin kaucewa tsaikon karatu da yajin aikin da ka iya shafar dalibai da harkokin ilimi baki daya.
You must be logged in to post a comment Login