Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

Iyaye su rinka fadakar da ‘yayansu illar Fyade- Ogenyi Onazi

Published

on

Dan wasan tsakiya na kungiyar kwallon kafa ta kasa Super Eagles, Ogenyi Onazi, ya buka ci iyaye a kasar nan da su rinka wayar da kan ‘ya’yan su Maza kan illar da yin Fyade ga ‘ya’ya mata yake da shi.

Onazi, ya ce a ‘yan kwanakin nan an samu yawan aikata Fyade ga ‘ya’ya mata a kasar nan wanda ya janyo da yawa daga cikin al’ummar kasar nan ke takaicin yawan samun matsalolon na Fyade a wannan lokacin.

Ya kuma ce matsalar Fyade na daya daga cikin abin da ke kawo masifa a kasa ta yadda masifu ke afkuwa a gurare daban daban a kuma rasa musabbabun abin da ya kawo su.

Onazi ya kara da cewa yakan ji bakin ciki a duk lokacin da ya samu labarin wani yayiwa wata fyade a kasar nan.

A don haka yake kara kira ga malamai da gwamnatoci da iya’ye kan su rinka gudanar da wani shiri na musamman a makarantun kasar nan da zai rinka wayar da kan mutane kan illar da fyade yake dashi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!