Connect with us

Labarai

Jami’ar FUD ta Jigawa ta nemi  haɗin kan ’Yan Sanda domin dakile ƙungiyoyin asiri a makarantar

Published

on

Jami’ar Tarayya da ke Dutse a Jihar Jigawa, ta nemi  haɗin kan Rundunar ’Yan Sandan jihar domin dakile tashe-tashen hankula da ayyukan ƙungiyoyin asiri da ake zargen wasu ɗalibai da aikatawa

Jami’ar ta bayyana hakan ne yayin ziyarar ban-girma da Mataimakin Shugaban Jami’ar, Farfesa Ahmad Muhammad Gumel, tare da shugabannin jami’ar da wasu ma’aikata suka kai wa sabon Kwamishinan ’Yan Sandan Jigawa, Tijjani Murtala, a hedikwatar rundunar da ke Dutse.

Farfesa Gumel ya ce haɗin gwiwa tsakanin jami’ar da ’yan sanda na da muhimmanci wajen musayar bayanan sirri, dakile aikata laifuka da kuma kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Ya kuma nuna damuwa kan bullar wasu ayyukan ƙungiyoyin asiri da sauran munanan ɗabi’u a tsakanin wasu ɗaliban jami’ar, yana mai cewa akwai bukatar daukar matakan gaggawa kafin lamarin ya yi kamari.

A nasa martanin, Kwamishinan ’Yan Sandan Jigawa, Tijjani Murtala, ya tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da aiki kafada da kafada da jami’ar domin tabbatar da tsaron ɗalibai da ma’aikata.

Rundunar ta kuma yi alkawarin ƙara sintiri, sanya jami’an tsaro a wuraren da suka dace, tattara bayanan sirri da ɗaukar wasu matakan tsaro domin tabbatar da zaman lafiya a jami’ar da kewayenta.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!