Labarai
Shugaba Tinubu ya tabbatar da cewa matatun man kasar nan za su koma aiki

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya tabbatar da cewa matatun man kasar nan za su koma aiki, inda ya ce gwamnati na sake tsara yadda za a tafiyar da su domin su samar da riba da amfani ga ƙasa.
Tinubu ya bayyana hakan ne a jiya yayin da ya karɓi bakuncin shugabannin ƙungiyar dallalan man fetur NUPENG a Fadar sa dake birnin tarayya Abuja.
Ya ce kasancewar matatar suna aiki ba yana nufin tana aiki yadda ya kamata, ya kuma ce gwamnati zata cigaba da sanya indo dan ganin an samar da riba da amfanin da aka gina ta a kai.
Shugaban Kungiyar, Salimon Oladiti, ya kuma roƙi Tinubu da ya kawo ƙarshen ɗaukar ma’aikatan wucin gadi a ɓangaren man fetur da iskar gas.
You must be logged in to post a comment Login