Connect with us

Labarai

Jami’ar Aliko Dangote ta ce za ta bude sashin koyar da fasahar hada magunguna da Kere Kere.

Published

on

Jami’ar kimiyya da fasaha ta Aliko Dangote dake garin Wudil, ta ce nan bada jimawa ba za ta bude sashin koyar da fasahar harhada magunguna da kuma Kere kere a Jami’ar.

Shugaban Jami’ar Farfesa Musa Tukur Yakasai ne ya bayyana hakan yayin bikin yaye daliban Jami’ar karo na biyar dake gudana.

Ya kuma ce, Jami’ar tana ci gaba da samun sahalewar hukumar kula da Jami’o’i ta Kasa NUC domin cigaba da inganta harkokin Ilimi a Jami’ar.

Da yake jawabi shugaban gudanarwar Jami’ar ta Aliko Dangote mai shari’a Abdu Aboki ya ce Jami’ar na kokari wajen ganin an yaye dalibai masu tarbiyya, hakan tasa ba sa yadda a aikata duk wani abu na rashin tarbiyyaba a makarantar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!