Labarai
Jam’iyyar ADC ta soki hukuncin kotu kan rajistar NDC

Jam’iyyar ADC ta bayyana damuwa kan wasu matakan da take zargin ana ɗauka kan jam’iyyun adawa a Najeriya, tana mai gargadin cewa hakan na iya jefa ƙasar cikin tsarin mulkin jam’iyya ɗaya.
Martanin na ADC ya biyo bayan hukuncin kotu da ya shafi batun rajistar jam’iyyar NDC, inda kotun tarayya da ke Lokoja ta soke wani hukunci na baya da ya umarci hukumar zaɓe ta Nijeriya (INEC) ta yi wa jam’iyyar rajista, tana mai cewa ba a saurari dukkan masu ruwa da tsaki a shari’ar ba.
You must be logged in to post a comment Login