Labarai
Wajibi ƴan APC su marawa Tinubu baya a 2027 – Gwamna Abba

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya ce ya zama wajibi ƴan jam’iyyar APC su marawa Tinubu baya a zaɓen 2027 domin ciyar da al’ummar ƙasar nan gaba.
A wata sanarwa da mai magana da yawun sa, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, tace Abba ya bayyana hakan ne yayin ganawa da zaɓaɓɓu da naɗaɗɗun jami’an gwamnati a Fadar Gwamnatin Kano.
Ya ce Kano za ta mara wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu baya domin samun nasara a zaɓen shugaban ƙasa na 2027, tare da umartar dukkan masu riƙe da muƙaman siyasa da ba suyi rajista a APC ba su gaggauta yin hakan.
You must be logged in to post a comment Login