Labarai
Ubandoma ya fice daga PDP zuwa jam’iyyar APC

Tsohon ɗan takarar gwamna na jam’iyyar PDP a Jihar Sokoto a zaɓen 2023, Mallam Sa’idu Umar Ubandoma, ya fice daga jam’iyyar tare da komawa jam’iyyar APC.
A cikin wata sanarwa da mai taimaka wa Sanata Aliyu Magatakarda Wamakko kan yaɗa labarai, Bashar Abubakar, ya fitar, an ce Sanata Wamakko ne ya karɓi Ubandoma cikin APC a gidan sa da ke Asokoro, a birnin tarayya Abuja.
Ubandoma, wanda ya taɓa zama Kwamishinan Kuɗi da Sakataren Gwamnatin Jihar Sokoto a zamanin gwamnatin Sanata Aminu Waziri Tambuwal, ya ce salon jagorancin Sanata Aliyu Magatakarda Wamakko da ayyukan ci gaban da Gwamna Ahmed Aliyu ke yi ne suka ƙarfafa masa gwiwar komawa Jam’iyyar ta APC.
You must be logged in to post a comment Login