Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Siyasa

Jam’iyyar APC ta karawa zababbun shugabannin shugabanninta wa’adin shekara 1

Published

on

Jam’iyyar APC mai Mulkin Najeriya ta karawa zababbun shugabannin ta da suka hadar da shugaban jam’iyyar na kasa Chief John Odigie-Oyegun wa’adin tsawon shekara guda.

Wannan na kunshe ne a wata sanarwa da kwamitin zartaswar jam’iyyar ya fitar a Abuja.

Sanarwar tace karin wa’adin zai fara aiki ne daga ranar talatin ga watan Yunin shekarar 2018.

A baya-bayan nan ne shugaban jam’iyyar na kasa Chief John Odigie-Oyegun suka yi wata ganawar sirri da shugaban kasa Muhammadu Buhari, biyo bayan rahoton da jagoran jam’iyyar na kasa Bola Tinubu ya mikawa shugaba Buhari.

Rahotanni sun bayyana cewa cikin rahoton ana zargin Chief John Odigie-Oyegun da yiwa yunkurin sasanta rikicin cikin gida da ya kunno kai a tsakanin mambobin jam’iyyar kafar angulu.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!