Labarai
Majalisar dokokin Kano ta buƙaci a gyara babban ɗakin karatu

Majalisar Dokokin Jihar Kano, ta karɓi ƙudirin neman a gyara tare da zamanantar da ɗakin karatu na Murtala Muhammad Library da ke nan jihar Kano.
Nabil Aliyu Daneji, Ɗan Majalisa mai wakiltar Ƙaramar Hukumar Birni ne ya gabatar da ƙudirin, inda ya ce ɗakin karatun na buƙatar gyara duba da yadda kayayyakin da ke cikinsa da kuma ginin wurin suka lalace.
Ɗan majalisar ya yi kira ga Gwamnatin Jihar Kano da ta ɗauki matakin gyara tare da zamanantar da ɗakin karatun, musamman ta hanyar samar da na’urorin kwamfuta da sauran kayan zamani da za su inganta ayyukansa.
Ƙudurin dai, ya samu goyon bayan ɗan majalisa mai wakiltar Ƙaramar Hukumar Ungogo, Sa’ad Aminu Sa’ad tare da bawa kwamitin ilimi zurfi da ya je don duba halin da ɗakin karatun ke ciki tare da gabatar da rahoto a gaban majalisar.
You must be logged in to post a comment Login